Sojojin Najeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 82, Sun Kama 198 a Mako Daya

uploads/images/newsimages/KatsinaTimes23022025_133630_FB_IMG_1740317689405.jpg

Hedikwatar Tsaro ta bayyana cewa dakarun sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda 82, tare da kama 198, tare da ceto mutane 93 da aka yi garkuwa da su a cikin mako guda.  

Daraktan Hulɗa da Manema Labarai na Tsaro, Manjo Janar Markus Kangye, ne ya bayyana hakan yayin da yake gabatar da sabbin bayanai kan ayyukan rundunar a ranar Juma’a a Abuja.  

A cewarsa, sojojin sun kuma kwato makamai 152 da alburusai iri-iri tare da wasu kayayyakin yaki da suka hada da. Bindigogi 86,  AK-47 guda 46, da kanana 18 da wasu 19 na gargajiya. Alburusai 2,040 na nau’uka daban-daban, ciki har da 1,165 na 7.62mm Special da 128 na 7.62mm NATO.  

Haka nan, dakarun sojojin sun cafke mutane 22 da ke da hannu a satar man fetur a yankin Kudu maso Kudu, tare da dakile asarar mai da kudinsa ya kai Naira miliyan 587.  

Bugu da kari, ‘yan ta’adda 41 sun mika wuya a yankin Arewa maso Gabas, tare da makamai da alburusai da suka hada da PKT gun, AK-47 da bindigar AK-101.  

Kangye ya tabbatar da cewa sojojin Najeriya za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a duk fadin Najeriya

Follow Us